IQNA

An Zabi Dan Kasar Chadi A matsayin Sabon Shugaban Kungiyar Kasashen Musulmi Ta OIC

22:56 - November 29, 2020
1
Lambar Labari: 3485411
Tehran (IQNA) an zabi Hussain Ibrahim Taha a matsayin sabon babban sakataren kungiyar kasashen musulmi ta OIC.

Jaridar Yeni Safak ta bayar ad rahoton cewa, an zabi Hussain Ibrahim Taha ne dan kasar Chadi a matsayin sabon babban sakataren kungiyar kasashen musulmi ta OIC a ranar jiya Asabar.

An zabi Taha nea  a lokacin kammala zaman taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobi na kungiyar, wanda aka kammala jiya Asabar a birnin Yamai fadar mulkin mulkin jamhuriyar Nijar.

Sanann kuma zai maye gurbin Yusuf Ahamd Usaimin babban sakataren kungiyar da wa’adinsa ke karewa, inda zai bar kujerarsa  a cikin watan Fabrairun 2021, yayin da kuma Taha zai karbi ragamar ayyukan kungiyar.

OIC dai tana a matsayin babbar kungiya a duniya, wadda take da mambobi 57 daga nahiyoyi hudu na duniya.

 

3938014

 

 

 

 

 

Wanda Aka Watsa: 1
Ana Cikin Dubawa: 0
Ba A Iya Watsa Shi: 0
Mua'zzam
0
0
Allah ya bashi ikon riko da gaskiya, da Kuma tabbatar da adalci a tsakanin al'ummam musulmai baki daya, ya Kuma Kare shi da sharrin Yahudu, Nasara da kuma yan uwansu na cikin musulunci wato masarautar Sa'ud!
Amin summa Amin.
captcha